PDP za ta bayar da takarar shugaban ƙasa ga yankin Arewa

PDP za ta bayar da takarar shugaban ƙasa ga yankin Arewa

Akwai matuƙar tsammanin jam'iyar PDP za ta bayar da takarar shugaban ƙasa a ɓangaren Arewacin Nijeriya a zaɓen 2023 in da za ta kai matsayin shugaban jam'iya a gefen kudu.

A lokacin taron shugabannin jam'iyar a ƙarshen sati sun sanar da cewa za su faɗi yanda karɓa-karɓar za ta kasance a zaman da za a yi ran 9 ga Satumban 2021.

Wannan ya zo ne kan faɗi tashin jagororin siyasar jam'iyar ke yi wanda yakai ga sanya 30 da 31 na Okotoba za a yi babban taron jam'iyar.

Zaɓen shugabannin jam'iyar zai cigaba duk da rigimar shari'ar da ake yi a kotuna.

Yankin Arewa maso Yamma har yanzu bai da zaɓaɓɓin shugabanni tun sanda aka shirya zaɓe bai yiwu ba kan rigimar Tambuwal da Kwankwaso abin jira a gani za a yi zaɓen kafin babban taro ko sai bayan taron.