Tinubu ya sanar da sabon albashi mafi ƙanƙanta ga maikatan Najeriya

Tinubu ya sanar da sabon albashi mafi ƙanƙanta ga maikatan Najeriya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da naira 70,000 a matsayin sabon albashi mafi ƙanƙanta ga ma'aikatan gwamnatin ƙasar.

Tinubu ya sanar da sabon albashin ne a ganawarsa da wakilan ƙungiyoyin ƴan ƙwadago na ƙasar a ranar Alhamis.

Ministan yaɗa labaru na Najeriya, Mohammed Idris ya sanar da manema labaru cewa "ina farin cikin shaida muku cewa a yau (Alhamis) ƙungiyoyin ƴan ƙwadago na Najeriya da Gwamnatin Tarayya sun amince da wani ƙari a kan naira 62,000 a matsayin albashi mafi ƙanƙanta.

Sabon albashin mafi ƙanƙanta da ake sa ran shugaban ƙasa zai gabatar wa Majalisar Dokokin Tarayya shi ne naira 70,000."

Baya ga ƙarin albashin mafi ƙanƙanta zuwa 70,000, shugaban na Najeriya ya kuma yi wa ma'aikatan wasu alƙawurra.

Kamar yadda ministan yaɗa labaru Mohammed Idris ya faɗa, "gwamnatin Najeriya za ta narkar da maƙudan kuɗaɗe a ɓangaren samar da kayan more rayuwa.

Gwamnatin za ta kuma ƙara zuba kudi a ɓangaren makamashi mai tsafta, tare da samar da ƙarin motocin bas masu amfani da man CNG."