Shugaba Buhari Zai Naɗa Wani Sabon Minista A Nijeriya 

Shugaba Buhari Zai Naɗa Wani Sabon Minista A Nijeriya 

Shugaba Buhari Zai Naɗa Wani Sabon Minista A Nijeriya 

Daga : Janaidu Amadu Doro.

Shugaban ƙasa Muhammdu Buhari ya miƙa sunan Mu’azu Jaji Sambo daga jihar Taraba a gaban majalisar dattijai domin naɗashi a matsayin sabon minista.

Shugaban majalisar dattawa Sanata Ahmad Lawan ne ya bayyana hakan lokacin da ya ke karanto wata takarda da shugaban ya rubutawa zauren a yau Talata.

Shugaba Buhari ya buƙaci majalisar dattawa da ta tantance tare da tabbatar da Ma’azu Jaji domin naɗa shi a matsayin sabon minista.

Tsawon lokaci bayan da Buhari ya saukar da ministocinsa guda biyu sai a yanzu ya aika sunan ɗaya daga jihar Taraba daga Kano ba a tura kowa ba har yanzu.