Ƙungiyar PDP Mandate Ta Miqa Masu Canja Sheka Sàma Da Dubu Ga Uwar Jam'iyyar PDP A Neja
Join our subscribers list to get the latest news, updates and special offers directly in your inbox
Daga Awwal Umar Kontagora, Minna.
PDP Mandate ta mika sama da mutum dubu daya yayan jam'iyyun APC, NNPP da PDM da suka yi canjin sheka daga jam'yyun su zuwa jam'iyyar PDP a karamar hukumar Bosso.
Tunda farko a bayaninsa, jagoran matasan PDP kuma jigo a kungiyar, Amb. Nura Hashim ya bayyana cewar wadannan jama'an sun gaji da wannan mulkin na APC tsawon shekaru bakwai da watanni talakawan jihar nan ba su san da akwai gwamnatin jiha ba, domin idan ka dubi yadda aka karya tattalin arzikin talakawa a jihar nan abin bakin ciki ne, garkuwa da mutane a gonakin su, tarwatsa karkaru ana farautar fan Adam kamar ana farautar bera a wannan gwamnatin muka gan shi, saboda haka PDP Mandate ta gabatar min da wasu 'yan jam'iyyu da suke rike da mukaman jam'iyya sun amince su dawo PDP dan mu yi aiki tare.
Kamar yadda muka gudabar da wannan taron yawon a karamar hukumar Bosso, haka za mu yawuta sauran kananan hukumomin jihar nan dan fitar da kitse daga wuta, a shirye muke mu yiwa jam'iyyar PDP aiki dan ganin mun samu nasarar babban zabe mai zuwa, muna kara jaddawa al'ummar jihar nan da yardar Allah idan mun dawo kuskuren da mu ka yi a baya ba za mu sake yin irinsa ba.
Alhaji Garba Danlami, shi ne shugaban PDP a karamar hukumar Bosso, da ya wakilci shugaban jam'iyyar ta jiha, Barista Tanko Beji. Yace batun dawowar wadannan al'umma a PDP abin a yaba ne domin mu da su manufar mu daya ce, itace dawo da martabar jihar nan ta hanyar mutunta tsarin dimukurafiyya.
Saboda daman yayan PDP da suka tafi cirani kuma sun fahimci gidan da suka bari nan ne mafi dacewa a zaman su, da wanda ya fara PDP 1999 da su da suka shigo yau, da su wadanda da suka dawo PDP yau duk daya ne a wajen mu.
Beji, ya bada tabbacin a wannan tafiyar ba wanda za a bari baya uwar jam'iyya za ta tabbatar ta tafi da kowa musamman a yanzu da ake sa ran fara yakin neman zaben 2023 ba da jimawa ba.
Daya daga cikin wanda ya jagoranci masu canjin shekar, Hon. Sani Ashiru Bazanga, yace dukkanin wadannan mutanen zangon farko ne da suka nemi dawowa PDP ta hannun jagoran mu, Amb. Nura Hashim a karkashin PDP Mandate kuma yanzu haka akwai wasu jigogin jam'iyyar APC da muke shirin karban su.
Hon. Abdullahi Sa'idu Pyawu, yace wannan ba abin mamaki ba ne, PDP tayi mulkin jihar nan kuma saboda zakuwa da jin dadi al'ummar jiha suka nemi canjin gwamnati wanda APC ta karba shekaru bakwai ke nan da watanni al'umma sun kosa jam'iyyar PDP ta dawo.
Kamar yadda na ji Ambasada Nura Hashim ya fada ne a jawabinsa, wannan gwamnatin ake cewa jiki magayi, kuma duk wanda bai godewa ni'imar Allah ba, ai dole yayi da nasani.
Taron wanda irin shi ne na farko da PDP Mandate ta shirya a sakatariyar jam'iyyar ta karamar hukumar Bosso ta taho da sabon salo domin akwai fuskokin wasu fitattun yan APC da har yanzu ba su bayyana ficewarsu ko cigaba da zama jam'iyyar ba.
Ya samu halartar 'yan takarkarun majalisar jiha da ta tarayya da ya shafi kananan hukumomin Bosso da Paikoro.
managarciya Oct 30, 2021 12 169
managarciya Feb 3, 2025 3 110
Maryamah Dec 14, 2021 2 87
Maryamah Dec 16, 2021 10 73
managarciya Jun 24, 2023 5 73
managarciya Nov 13, 2023 0 550
managarciya Nov 12, 2023 0 346
managarciya Nov 12, 2023 0 335
managarciya Nov 12, 2023 0 416
managarciya Nov 11, 2023 1 702
managarciya Nov 3, 2021 0 611
A wani hasashen an danganta samun ƙabilar Hausawa da auratayyar al’ummatai daga...
managarciya May 10, 2024 0 478
Farfesa Aisha Bawa ita ce mace ta farko a sashen ilimin nazarin Tarihi a Jami'ar...
managarciya Jan 11, 2023 0 358
Amsa: Kwarai da gaske,ai Bahaushe ya yi magana yace ciwon 'ya mace na 'ya mace ne,don...
managarciya Jan 23, 2024 0 359
managarciya Jan 1, 2024 0 299
Wasu mutane na ganin tun farko gwamnti ta yi ragon azanci don bai kamata ta sayi...