PDP ta lashe gaba ɗaya kujerun ciyamomi da na kansiloli a zaɓen ƙananan hukumomi a Osun

PDP ta lashe gaba ɗaya kujerun ciyamomi da na kansiloli a zaɓen ƙananan hukumomi a Osun

Jam’iyyar PDP ta lashe dukkanin kujerun ciyamomi 30 da na kansiloli 332 a zaben kananan hukumomin da aka gudanar a jiya Asabar a Osun.

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar, OSSIEC, Hashim Abioye, ne ya sanar da sakamakon zaben a gidan talabijin mallakin gwamnati, Osun Broadcasting Corporation, OSBC, a Osogbo.

Mista Abioye ya bayyana cewa jam’iyyun siyasa 18 ne suka shiga zaben amma PDP ta lashe dukkan kujerun.

Ya kuma ce an yi zaɓen bisa bin doka da ka'ida.