Kotu Ta Rusa Zaɓen Fitar Da Gwanin Ɗan Takarar Gwamnan  Jam'iyar APC A  Jihar Taraba

Kotu Ta Rusa Zaɓen Fitar Da Gwanin Ɗan Takarar Gwamnan  Jam'iyar APC A  Jihar Taraba

Daga Ukasha Ibrahim.

Babban kotun tarayyar wacce ke da zamanta a jalingo  fadar gwamnatin jihar Taraba ta rushe zaben fitar da  gwanin na dan takarar gwamna a karkashin jam'iyar ta APC 

Mai shari'a  Simon Amobeda  ya yanke wanan hukuncin ne ayau Talata  inda ya rushe zaben fidda gwani na  gwamnan jihar wanda jam'iyar APC ta gudanar a watannin da suka wuce inda dama jami'yar ta sanar da sanata  Emmanuel Bwacha amatsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar 

Mai shari"ar ya sanar da rushe wanan zaben kamar yadda daya daga cikin "yan takarkarun da suka fadi a awanan zaben  mai suna Chief David Sabo Kente ya shigar da kara 

Sanan alkalin ya bukaci hukumar zabe mai zaman kanta da tasake gudanar da zaben fitar da gwanin  na 'dan takarar gwamnan jihar Taraba karkashin jami'yar APC nan da kwana 14 masu zuwa .