Sanata Adamu ya sanar da Ahmed Lawan a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na maslaha

Sanata Adamu ya sanar da Ahmed Lawan a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na maslaha

 

Rahotanni da ke fitowa da ga Abuja a yanzu sun bayyana cewa Shugaban Jam'iyar APC na Ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya sanar da Ahmed Lawan, Shugaban Majalisar Dattawa a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na maslaha a jam'iyar.

Adamu ya bayyana hakan ne a taron gaggawa na Kwamitin Ƙoli na jam'iyar, NWC a yau Litinin a Abuja.

Sai dai kuma Adamu ya ce sauran ƴan takara irin su Asiwaju Bola Tinubu; Yemi Osinbajo;  Kayode Fayemi da David Umahi za su iya shiga zaɓen fidda-gwani da za a yi gobe a Eagle Square, Abuja.