Jirgin Yaƙi Ya Yi Luguden Wuta Ga Mahara A Sakkwato Da Katsina
A daya daga cikin hare-haren, jiragen yakin sun lalata sansanin wani dan ta’adda da ake kira ‘Gajere’ inda aka kashe yaransa 34, wasu kusan 20 kuma sun samu raunukan harbi
Rahotanni sun ruwaito mutanen da ke zaune a yankunan da aka kai hare-haren suna bayar da labarin yadda suka ga maharan na ta tserewa, yayin da wasu suka fake a wata makarantar firamare da ke kauyen Bafarawa.
A Jihar Katsina an gano yadda jiragen yakin Najeriya suka yi ta ruwan bama-bamai a maboyar maharan a dajin Rugu da ke da iyaka da Karamar Hukumar Kankara ta Jihar Katsina a tsakanin ranar 30 ga watan Satumba da 3 ga watan Oktoba, 2021.