ƘADDARA TA RIGA FATA: Fita Ta 19
NA MARUBUCIYA:-
AUNTY NICE✍🏼
@wattpad AuntyNice.
SADAUKARWA GA ƳAƳA NA HASKEN ZUCIYA TA:-
NABEELAH ARABI
NUHU ARABI
SHAFI NA 19📑
__📖 Baki na a buɗe na ƙurawa kyakkyawan fuskar shi ido bana ko ƙyaftawa, yana gama maganan ya buɗe idon shi ya ɗaura su a kan fuskata.
“Ya Rabbi”na furta a bayyane, domin ban taɓa ganin kyaun Dr irin na yau ba, hannuna na fara shirin ƙwacewa daga nashi hannun, don naji bazan iya tsayawa a inda yake ba yau kam, sannan ban san wacce irin amsa zan bashi ba.
“Ki nutsu ki bani amsan tambayana kinji babyn baby” ya faɗa cikin muryan shi da ban taɓa jin shi da ita ba sai yau.
“Alhamdulillah” na faɗa a zuciyata ganin Amal da ke tahowa inda muke, fuskanta ɗauke da murmushi ta gaida Dr, wanda har lokacin yaƙi sakin hannu na, waya na ta miƙo mun tana cewa, “gashi Hummy kusan 2 miss call darling forever ya miki, shi ne nace bari na kawo miki ko nasamu ya barni nayi aikina”, ta faɗa tana munafukin murmushi.
A dole ya sake hannu na domin na karɓi phone ɗina, ina karɓa wani call ɗin yana shigowa, saida na kalli Dr Hussain a fakaice tukun na ɗaga ƙiran.
“My luv kayi haƙuri mana ina wurin lecturer mune yana gwada mun karatu”, na faɗa wa Faisal bayan irin ƙorafin da ya fara akan na yar da wayan ba kusa da ni ba, shi kuma Dr Hussain ya kasa yin komai sai ƙura mun idon shi da yayi kawai.
“don Allah rufa mun asiri kayi zamanka a school, idan ka taho nan kuma ae soyayyanka bazai barni nayi nawa karatun ba, gashi next week test babu iyaka muke da su”, na faɗa mishi da muryan lallashi.
Ratsa gefe na yayi zai wuce nayi sauri na riƙo hannun shi, ban kuma kalli inda ya ke ba, ban kuma daina wayana ba, ina gamawa na juyo da murmushi na dube shi, “Drn mu bansan wani irin so muke yiwa juna ba nida Faisal? Kasan wai saboda ban ɗauki wayan shi akan lokaci ba da har yayi niyyan tahowa inda nake, gaskiya da yazo da babu abinda zai saka na iya fahimtan karatun da ake mun”, na faɗa ina nuna ban ma fahimci wani hali Dr ya shiga ba.
Ƙwace hannun shi yayi ya wuce ya barni a wurin, dariya nayi na bishi da gudu-gudu, har zai shige gidan shi na sha gaban shi, na lanƙwasa kaina gefe kaman me neman a yafe mata, ina murmushi nace, “Drn mu yaushe zamuyi karatun? Ko sai after munyi dinner zaka gwada mana”?.
“Allah ya kaimu” ya faɗa ya wuce ya barni inata dariya a ɓoye, ina shiga parlon mu da gudu naje na rungume Amaal, dariya ita ma takeyi muka gama zagaya wurin tukun muka zauna, “bani labari babyn Dr”, ta faɗa muna dariya.
Bayan nagama bata labarin duk abinda ya faru, sai ta ɗaga kanta kaman mai tunani, chan ta sauƙo da kanta tana kallo na tace, “mistake ɗaya Hummy, baki ce mishi komai ba sai kika fara bashi labarin soyayyan ku da Faisal, hujjah”?
Dariya nayi na miƙe tsaye ina kallon ta, “17yrs nake fa Amaal, Drn mu 40yrs yake, kinga akwai 23yrs a tsakanin mu, yaushe zan tura mishi tunani na kusa da na shi? ae bazai dinga mun uzuri ba a rayuwa kullum zai mun kallon mai hankali da shekaru, amma yarinta na kullum zai zamo abinda zai banbantani da sauran mata, sannan zaina haƙuri da ni a kowani lokaci, kinga shi fah yanzu zaiyi tunanin ban fahimci abinda yake nufi ba, toh zaije ya zauna yayi ta wasa ƙwaƙwalwar shi da lissafin wani hanya zai sake bina da shi, kuma wani hanya zai ya kuce mun wannan yaron a raina, kuma ko daga baya bazaice shi kaɗai na taɓa so ba, dole shima ya haɗu da rival ta wurina, ki barshi ni bazan bashi amsa ba, yanayina kaɗai zai wadatar da shi, har ya aminta babu wani a zuciyata sama da shi, amma a hankali”, na faɗa bayan na koma gefen Amaal na zauna.
“hmmm shiyasa akace ko wacce mace da irin nata kissan ake haihuwarta da shi inji kakarmu, babu wacce ka isa ka zaunar da ita ka koya mata kissa, saidai ka tunatar da ita kawai, domin ko ka koyawa mace abinda zatayi, toh bazatayi exactly irin yadda aka gwada mata ba, sai nata baiwan ya shiga ta sarrafa shi ta wani wurin daban, kaman yadda yanzu kikayi, bayan Ummi ta gwada miki nata hikiman, nima na gwada miki, sai kika yi naki hikiman, gaskiya ƴar’uwata kin burgeni, Allah ya barki da Drn ki ɗan tsoho kusha soyayyah”, ta faɗa tana dariya na.
Nima dariyan nayi nace, “musha soyayyah yayi ta goyani ina jin daɗi”.
Wayata na ɗauka nayi dialing number Dr ina ɗan murmushin shaƙiyanci, yana ɗauka nace, “hello Dr na baka shigo munyi dinner ba, kuma wallahi yunwa na keji”, na faɗa kaman zan mishi kuka.
“ku ci kawai bana tare da yunwa”,
ya faɗa ya kashe wayan, kallon Amaal nayi ina dariya nace, “bari naje nayi biko”.
Kaman bazai buɗe mun ƙofan shi ba bayan nayi knocking, yana buɗewa na ratsa gefen shi na wuce cikin parlon na tsaya ina duban shi babu dariya a fuskana, shima ƙura mun ido yayi yana mun wani irin kallo.
“Dr meyasa bazaka zo muci abincin ba”?
“Nace miki bana tare da yunwa, kwanciya ma zanyi zo ki wuce ki tafi, na hanaki shigowa nan ae”.
Wucewa nayi na nemi wuri na zauna ina kallon TV da ake news, kallona ya tsayayi bai ce komai ba, ganin haka yasa na dube shi nace, “ka rufu ƙofan mana kazo mu zauna, tunda kace baka jin cin abinci nima ae bazan iya ci ba, kuma yau anan gidan zan kwana tunda kai yayah nane, kuma uncle ɗina ne”, na faɗa ina shirin miƙewa na kwanta a wurin.
Da sauri yazo ya tsuguna a gabana yana kallo na, ƙura mun ido yayi kafin yace, “saboda me zaki kwanta anan? Baki tsoron komai ne kam ke”?
Tashi nayi na zauna, na rufe idona naƙi kallon shi, domin bana jin daɗin ƙura mishi ido, “ban taɓa tunanin zaka iya cutar da ni ba, nayi imani da Allah yadda Daddy na zai kareni ya kare mun mutuncina haka kaima zakayi, ina ji ajikina zaka iya sadaukar da rayuwarka domin tsare mun mutuncina, kuma koda a jikin ka zan kwana zaka fi kowa tsare mun mutuncina, saboda haka bani da shakku akanka”.
Ajiyan zuciya ya sauƙe mai ƙarfi, sunkuyar da kanshi ƙasa yayi bai iya cewa komai ba, hannu na saka na riƙo hannun shi, wanda yayi sauri ya ɗago kanshi yana duba na, gaba ɗaya ganin idon shi sai naji ya bani tausayi, a hankali na furta, ” Dr nah! Nafi son na ganka kana murmushi, amma yau kaƙi kayi, narasa me ya sameka, sai naji bana jin daɗin komai a rayuwar, don Allah me kake so”?
Nunani yayi da kanshi, duk da na fahimci yana nufin ni yake so saboda tambayan dana mishi me yake so? Amma sai nayi kaman ban fahimta ba, sai na buɗe ido nace, “kana son na fita nabaka wuri”?
Runtse idon shi yayi da ƙarfi, alamar ba haka yake nufi ba, jijjiga hannun shi nayi da ƙarfi nace, “wayyo Dr na ko na ƙira Dr Abdallah ya duba mun kai ne? Dr na baka da lafiya ne”?
“Abdallah, Faisal, duk kinfi damuwa dasu sama da ni ko”? ya faɗa da wani yanayi kaman na yaro ɗan 20yrs.
Tashi nayi na tsaya, shima tashi yayi ya tsaya ya ƙura mun ido, ni kuma turo bakina nayi gaba nace, “Faisal masoyina ne, Dr Abdallah friend ɗin Amaal ne, kai kuma na damu da kai ne, ina jin ka sama da komai da kowa, saboda haka zo mutafi bana son musu muje muci abinci sai kamun karatu”, na faɗa ina tafiya hanyar waje, babu musu kuwa ya biyo ni.
Duk wani text da zamuyi munyi shi, Dr Hussain ɗina babu abinda ya bari ya shige mana duhu, duk da rabin karatun zolayan shi nakeyi, na hana shi saƙat, ita kuma Amaal banda dariyan mu babu abinda ta keyi, idan na fara shirmena ajiye komai ya keyi ya ƙura mun ido, har sai Amaal ta gama dariyan ta tayi mun masifa tace nabar mu muyi karatu, amma shi kam baya iya hanani komai sai yadda naso.
Wataran ana karatun zan tsaya nace, “Dr mu nikan muje musha ice creem, kaina ya daina ɗaukan karatun”, haka zai tattara mu muje, idan munje kuma na dinga mitan mata suna kallon shi, kuma nayi kane kane a kusa dashi ina hararan su, haka zai yita kallona bazai ce uffan ba.
Watarana kuma ana karatun ƙiran Faisal zai shigo don neman tsokana zan ɗauka nayita maganan soyayyah, har na miƙawa Dr nace dole sai sun gaisa, toh irin wannan lokacin baya iya daurewa, tashi yakeyi ya barmu, kuma naƙi nuna wani abu ya faru, haka zanyi ta binshi har sai ya sake dolen shi.
Gashi yanzu na tsiro da wani hali sai naga muna school lokacin da muke break zan kira shi na fara damun shi da fitinan ni sai naganshi, na dinga mishi kaman zanyi kuka, babu yadda ya iya dolen shi yake zuwa ƙofan class ɗinmu, ni kuma ina fita zan je nayita gaya mishi magana kaman na soyayyah amma a fakaice, ” Dr mu kasan bana jin daɗin komai idan ban ganka ba, wallahi ɗazu ma har saida nayi hawaye fa”,
“toh me yake saka ki son ganina”? Ya tambayeni bayan ya jingunu da jikin wani mota, ina binshi da murmushi nace, “nima fah ban sani ba, shine nake son kagaya mun, Dr nah nifah so nakeyi kayita goyona fa, zakayi”?.
Dariya yayi ya ƙura mun ido yana ta cizon lips ɗin shi, rufe ido na nayi alaman naji kunya nace, “ni idan kana kallona sai na dinga jin wani iri”.
“Don Allah me kike ji baby nah”? Ya tambayeni da sauri.
Dariya nayi nace, “sai ka goyeni tukun na gaya maka”.
“Baby toh kinƙi ki yarda mu rayu dake ballantana na dinga goyonki kullum, ki amince mana”.
Ina kallon shi nace, “wai baby a ina zamu rayune ni dakai? Bayan yanzu ma kullum muna tare baka taɓa goyo na ba”?
“Idan mun koma gida zan gaya miki, kinga nan school ne idon kowa yana kanmu”, sallama yamun ya tafi office, ni kuma na koma class.
Muna gama dinner muka fito da books ɗinmu ya ɗan koya mana abinda ya sha mana kai, muna gamawa na matso kusa dashi nace, “Baby nah me zaka gaya mun ɗazu”?
Ɗago kai yayi ya kalli Amaal, sai ya maida kallon shi kan TV, ganin haka Amaal ta tashi ta wuce ɗakin mu tana ta dariyan drammer mu.
Juyowa yayi ya kalle ni, sai naji kaman bazan iya zama.kusa da shi ba, ina ƙoƙarin matsawa naji ya riƙo hannu na da sauri, kasa kallon shi nayi kawai sai na turo bakina gaba, “Babyn baby ina son mu rayu irin na ma’aurata, ina nufin mu rayu a ƙarƙashin inuwar aure, ina so nazama abokin rayuwar ki ni kaɗai, kuma kizama tawa kema, toh a wannan lokacin kullum kike so zan dinga goyonki har sai kince kin gajji”.
Kasa ɗago ido na nayi domin na kalle shi, duk sai naji yau yamun wani girma, ina so na gudu shi kuma ganin haka sai ya ƙi sake hannuna, “Baby ki yadda dani don Allah, na rasa abubuwa masu muhimmanci a rayuwata, banida kowa sai ke, banida family, bani da komai, ki taimakeni mu zauna a inuwa ɗaya nima na samu family kafin na bar duniya”.
“kana da family, bakana da Ummi da Abba ba, kana da Hassan da Aisha, kuma ni ƴar yarinya yayah zanyi na aure ka? Kamun girma, kuma ae bakace Hummy ina sonki ba, shi kuma Faisal kullum sai yace yana sona, ni yaro nake so kamun tsufah, za ayita mun dariya ne, Amaal ma dariya zata mun”.
Lumshe idon shi yayi kaman bazai buɗe ba, chan kuma sai ya buɗe yana murmushi, wanda har abin yaso ya bani tsoro, na ɗauka masifah zai mun sai naga sai murmushi yakeyi, Hannun na ya ɗaga ya ɗaura a dai-dai saitin heart ɗinshi, gaba na naji ya faɗi saboda yadda heart ɗinshi yake bugawa da sauri-sauri, ajiye hannu na yayi a ƙasa sannan ya miƙe ya zura hannun shi a aljihun wandon shi ya juya mun baya, har saida yaje zai fita tukun ya tsaya batare da ya juyo ya dube ni ba yace.
“Abinda kike so kiji na miki alƙawari zakiji shi a wurina har sai ya hau kanki, na daɗe da sanin ga abinda kike so kiji daga gareni wanda ke baki san kina cikin yanayin hakan ba, amma na miki uzuri saboda ƙananun shekarunki, HUMMAIRAH tun ranan da na ganki wannna bugun zuciyata ɗin yaƙi daidaituwa, kuma tunda ga ranan na sakawa raina keɗin kece mahaɗin zuciyata, shiyasa ganinki yasata ta fara aikin da yake so ya fi ƙarfinta, kece ƙaddaran da ta gifta rayuwar mutane da dama, kece ƙaddarar da ta raboni da iyayena da ƴan uwana, kece ƙaddarar data raboni da soyayyar ahalina, kece ƙaddarar da zata sake haɗa ni da farin ciki na, kada kiyi duba da shekaruna, ina so kiyi duba na dacewan masu mabanbanta shekarun da sukayi, shi kaɗai zai baki nutsuwa da samun kwanciyar hankalin ki domin ki rayu a inuwa ɗaya da mai miki”…. Sai ya yi shiru, daga baya ya buɗe ƙofar parlon ya fita.
SALAMATU ABUBAKAR, (SALMA D.O)
tare da
ZAINAB ALƘALI (ZEE GOMBE)
wannan shafi na kune ƙannena, domin nuna muku irin godiyata da jin daɗina na yadda kuke nuna jin daɗin ku akan book ɗinnan, Allah ya albarkaci rayuwar ƴaƴanku, nagode Allah ya bar zumunci




