Jam’iyyar ADC a jihar Kebbi ta ce shari’ar da ake yi wa tsohon Ministan Shari’a kuma tsohon Antoni-Janar a zamanin mulkin Buhari, Abubakar Malami, SAN, tana da nasaba da siyasa, kuma ba za ta hana shi ci gaba da shirye-shiryen neman takarar zaben 2027 ba.
Jam’iyyar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar bayan taron shugabanninta a Sokoto, inda ta jaddada cewa za ta ci gaba da mayar da hankali wajen kokarin kayar da jam’iyyar APC mai mulki a babban zaben 2027.
ADC ya nuna gamsuwa cewa Malami zai iya kayar da APC a zaɓen 2027 saboda karɓuwar da ya samu a tsakanin mutanen jihar Kebbi.






