Home Uncategorized Sanatan Kaduna ya tsallake Rijiya da baya

Sanatan Kaduna ya tsallake Rijiya da baya

9
0

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kaduna, Muhammad Rabiu, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan zargin yunkurin kashe Sanata Usman Lawal (PDP Kaduna-Central).

Umurnin binciken na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Mansir Hassan, ya fitar ranar Alhamis a Kaduna.

Hassan ya ce, “’Yan sanda ba su san da yunkurin kashe Sanata Usman Lawal ba.

“An jawo hankalin hukumar ne ga wani buga a shafin Facebook na Sanata Lawal Usman.

Ya yi ikirarin cewa ya tsallake rijiya da baya a wani yunkurin kashe shi da wasu ‘yan daba suka yi a wani wurin da har yanzu ba a san ko su waye ba a Kaduna ta Arewa a ranar Laraba, kuma ba a bayar da lokacin faruwar lamarin ba.

Daga Abbakar Aleeyu Anache

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here