Home Uncategorized Muhimman Bayanai  Game da Sabon Shugaban Jam’iyyar PDP Na Kasa

Muhimman Bayanai  Game da Sabon Shugaban Jam’iyyar PDP Na Kasa

7
0

 

Ba sabon labari ba ne cewa majalisar gudanarwa ta PDP ta nada Umar Iliya Damagum a matsayin sabon shugaban jam’iyya na riko. 

Daily Trust ta fitar da rahoto game da abin da aka sani a kan rayuwa da siyasar Ambasada Umar Iliya Damagum wanda zai rike jam’iyyar PDP. 
Wanene shugaban rikon kwaryar:
  A ranar 10 ga watan Agustan 1963 aka haifi Umar Iliya Damagum, hakan yana nufin a shekarar nan zai cika shekaru 60 a Duniya.
 An haifi Umar Ililya Damagum ne a garin Damagum wanda yanzu haka yana karkashin karamar hukumar Fune a jihar Yobe. 
 ‘Dan siyasar ya yi firamare akauyensa daga 1971 zuwa 1977, daga nan ya tafi Maiduguri a jihar Borno domin yin karatun sakandare.
 A shekarar 2003, Damagum ya sake komawa jami’ar da ke kusa da shi domin yin digirgir, a nan ya samu digirn M. BA na ilmin kasuwanci. 
 A lokacin Gwamnatin Olusegun Obasanjo, ‘dan siyasar ya zama Jakadan Najeriya zuwa Romaniya, ya rike kujerar daga 2004 zuwa 2007. 
 Damagum ya nemi zama Gwamnan jihar Yobe a karkashin PDP a 2019, amma Mai Mala Buni ya doke shi, ‘dan takaran bai je kotu ba. 
 Bayan ya sha kashi a zaben sabon Gwamna, Ambasada Damagum ya fito takarar mataimakin shugaban PDP na kasa, kuma ya yi nasara. 
 Kafin ya zama shugaban jam’iyya na rikon kwarya, Damagum shi ne babba a cikin mataimakan Iyorchi Ayu a NWC, yana wakiltar Arewa. 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here