*NA MARUBUCIYA:-*
*AUNTY NICE*
*@wattpad AuntyNice.*
*SADAUKARWA GA ƳAƳA NA HASKEN ZUCIYA TA:-*
*NABEELAH ARABI*
*NUHU ARABI*
*SHAFI NA 14*
*MUM SAYYEED YADDA BAKI GAJJIYA DA JINJINA MUN, HAKA NIMA BA ZAN TAƁA GAJIYAWA DA BAKI ƊAN ƘARAMIN KYAUTANA NA SHAFI BA, DUK DA NASAN BA MAI YAWA BANE AMMA KIYI HAƘURI DA SHI, NA BAKI WANNAN SHAFI KYAUTA MUM SAYYEED, ALLAH YA BARMU TARE*
* Kaman bazan yi magana ba kawai na zuba mishi ido, can nace, “Toh ni ai ka zama Uncle ɗi na, kuma ai kamun girma ace kai boy friend ɗi na ne, ai Daddy idan yaji ina da boy friend ranshi zai ɓaci”.
na faɗa ina lanƙwasa kai na ina kallon yadda ya ƙura mun ido.
“Na ji abinda ki ka ce, nima nasan tunanin ƴan class ɗin ku baya gaya musu gaskiya, ke ai baki wuce ƴar ciki na ba da nayi aure da wuri,
dama ina son naji me zaki gaya musu idan kin koma class ɗin ne, saboda haka koma kice musu ni Baban ki ne”.
ya faɗa yana kama hanyar barin wurin.
Da ɗan gudu na bishi a baya ina cewa, “Dr’n mu to egg ɗin fa? Kafasa ci ne?”.
“Bana da sha’awan shi yanzu, ki koma bana son damuwa yanzu”.
ya faɗa tare da barin wurin da sauri.
Na daɗe a tsaye a wurin ina mamakin yadda ya ɗaure fuska lokaci guda, ya kuma juya ya tafi kaman bai san da ni ba a wurin, haka na ƙara ci tsayuwa na na juya na koma class raina a ɓace.
Ina shiga Ezeh ya zo kusa da ni ya zauna, hannu ya saka ya buɗe text book ɗin *TAXATION* ko tambaya na komai akan Dr bai yi ba, kawai bayani ya fara mun akan in da na tambaye shi ban gane ba, muna cikin yi sai ga Vicky, zama tayi kusa da ni tana murmushi, can ta tambaye ni, “ya ya Amal da jiki?”.
bayan mun yi gaisuwa ta ce da yamma zata je ta duba ta, ni kuma na gaya mata hospital ɗin da Amal ɗin ta ke, daga nan muka maida hankalin mu kan karatun da mu keyi.
Ƙaran takun takalmi muka jiwo, da sauri na ɗago na dubi mai shigowan, sanye da takalmi mai tsinin gaske, *Eesha* wannan ƴar india ne wanda ta ke ɗaukan mu *TAXATION* kuma ƙawar Dr Khadijah ce, sun yi kyau sosai, sai dai Dr Khadijah tafi kyau, ita kuma Eashaa tafi gayu, irin kallon da naga tana mun yau sai ya saka ni na kasa samun nutsuwa a class ɗin.
gashi ita ma kaman haɗin baki sai jeho mun quetions masu girma ta ke tayi, amma ko kaɗan basu ban tsoro ba, yadda nake bada amsan sai da ta tsaya wuri guda ta ƙura mun ido, can tace.
“Dr Hussain meye relation ship ɗin ku da shi?”.
Ban san ya ya aka yi ba sai samun kaina nayi da ce mata, “Uncle ɗi na ne, don shi ƙanin Dad ɗi na ne”.
“To me yasa yake yawo da ke? Kuma naga baya sakewa kowa fuska ya mishi murmushi amma ke yana miki? Kin tabbatar the same parent su ke da Dad ɗin ki ko kuma cousins ne?”.
“The same parents su ke da Dad ɗina, Dr Hussain ne ƙaramin su, sai Aunty Aisha, ita muna kama da ita, shi kuma yana kama da Dr Hassan”.
lokaci ɗaya naji na mata ƙarya don su rabu da ni, tun da naji yace ina kama da Aisha sai na gaya mata hakan.
Murmushi tayi tana kaɗa kanta alaman ta yarda, sannan tace, “me yasa Dr Khadijah Khan tace ki same ta a office ɗin ta baki je ba?”.
Tsuru-Tsuru nayi da ido, can kuma sai wani dabaran yazo mun da sauri nace,
“Dr’n mu yace na daina yawon zuwa office, na ce mishi tace naje yace mun no, bai yadda naje ba, amma ita ta tambaye shi tun da yana son ta zai yadda”.
Murmushi tayi ta matso in da na ke yadda ba maijin mu tace,
“ya ya ki ka san Dr yana son Khadijah?”.
Juya ido na nayi kaman wata mai shirin yin bacci nace, “shi ya gaya mun tana da kyau, bai taɓa ganin mai kyau irin ta ba”.
Murmushi ta sa ke yi tana duba na, “har ke duk kyaun ki bai gani ba sai na Khadijah?”.
Turo baki na nayi gaba nace,
“shi ai ko sister’n shi Aisha bai taɓa cewa tana da kyau ba, ballanta na ni, amma ita Dr yana gaya mun tana da kyau kuma ai wife ɗin shi ce yace mun”.
Jin haka ko ɓata lokaci Eashaa ba tayi ba ta fita da sauri tayi office ɗin Dr Khadijah, daga gani zata isar da saƙo ne wa Dr ƙawar ta.
Ni dai daɗi na mun rabo da su lafiya, sai suje suyi ta damuwar su a tsakanin su da Dr.
Lokacin break ya yi ni dai ban so ba haka na fita na sayi coke na sha, sannan naje nayi sallan azahar a mosque.
Lectures ɗaya muke yi bayan mun dawo a break, saboda 2:30pm muke ta shi, haka aka yi muna tashi kai tsaye na wuce gida.
Sallah nayi sannan na yi wanka, ina fitowa da sauri na shirya na fita domin zuwa duba jikin Amal, ina fitowa naga motan Dr Hussain alaman yana gida, hararan gidan shin nayi, sannan na murguɗa wa gidan baki na wuce na fita abuna.
Ina shiga ɗakin da aka kwantar da Amal na same ta zaune suna ta hira da Abbu da Ummi, sai dariya Amal ta keyi kaman bata yi jinya ba, wuri na samu na zauna na gaida su Abbu, sannan na tambaye su me zasu ci naje nayi mana take away?
Ummi ce ta miƙo mun wani ledan Mr Bigs, wanda na buɗe naga fried rice ne a ciki sai queter kaza, tana murmushi tace,
“ai tun wurin 2:00pm Dr Hussain ya kawo mana abinci, yace ke sai kusan 3:00 zaki shigo, saboda haka gana ki ma, mun gode mishi da ɗawainiyan shi a gare mu wallahi”.
Haka na zauna ina cin abinci na hankali kwance, ita kuma Amal sai zolaya na ta ke tayi wai, “ina Dr’n ki ne baby?”.
tana yi tana dariya, amma ni ko kallon ta ban yi ba, Abbu ne kawai ya ke ta taya ta dariyan Ummi kuma tana ta mata mitan ai zasu tafi su bar ta da ni ae, kuma tana bayan nima na rama abinda ta mun.
Wurin 6:00 Dr Abdallah yazo ya bamu sallama, yana cewa Abbu jikin da sauƙi sosai, sai dai duk bayan 2wks ya kamata tana zuwa follow-up, haka muka tattara kayan mu Dr Abdallah ya maida mu gidan, sannan ya dube ni yana murmushi yace,
“ki gaida Yayan ki kuma friend ɗin ki”.
ya faɗa yana mun murmushi, ni dai ko kula shi ban yi ba, haka muka shige gidan muka barshi da Abbu suna tattaunawa.
Muna sallan magrib na shiga kitchen, in da Ummi ta biyo ni, amma nayi ta roƙan ta dole ta fita ta barni, cous-cous na dafa wanda ya yi green, domin yaji food colour, sannan nayi vegetable soup wanda hanta yaji kacha-kacha a ciki, juice kala biyu na mana, ɗaya 5alive na mana, ɗaya kuma Apple ne kaɗai nayi blanding wa Amal.
Ina gamawa na wuce ɗaki nayi sallah, ina fitowa naga Abbu suna zaune da Dr Hussain suna ta magana a hankali a tsakanin su kaɗai suke jin abinda suke faɗi, gefe kuma Ummi ce da Amal ke zaune suna kallo, Amal ta kwantar da jikin ta a kafaɗan Ummi.
Shirya abincin nayi akan dinning, sannan na musu maganan su zo suci abincin, Amal ce ta fara ƙarasowa tana mun magana a hankali dai-dai kunne na tace, “Ke za kiyi saving Dr ko?”.
Tana faɗa taja kujera ta zauna tana murmushin shaƙiyan ci.
Hararan ta nayi cikin wasa nace, “to sannu Mama na”.
Dariya tayi mai sauti lokacin kowa ya zauna har shi Dr ɗin, “ni na isa na haifi zabgegiyar budurwa mai tashen farin jini irin ki? Wacce ni ai nayi kaɗan”.
Ta faɗa tana saving kan ta tana ta dariyan ta.
“To ku mana shiru muci abinci, idan yaso sai ku tashi daga in da ku ka tsaya”.
Ummi ta faɗa tana zubawa Abbu abinci, bayan ta zuba nata ta turawa Dr shima ya zuba.
Wurin gaba ɗaya ya yi shiru baka jin komai sai sautin ƙaran TV sai kuma ƙara spoons ɗin mu, kowa ya maida hankali kan abinda ya keyi, gashi daga ganin abincin ya yi daɗi, sai bin kowa da ido na ke yi, can nace.
“Abbu amma dai abincin nan ya yi daɗi ko?”.
Girgiza kai kawai yake tayi, “Doughter ban taɓa cin cous-cous da ya mun daɗin wannan ba, har tunani na ke yi ko zaki gwada wa Ummin ko yadda ki ka yi, idan mun koma ta na yimun”.
Dariya nayi tsabar daɗin jin abinda ya faɗa, ina kallon Ummi nace, “Ummi kema ya miki daɗi?”.
Tana murmushi tace, “sosai ma, don ni ban damu da cous-cous ba, amma daga yau nima zan dinga yi saboda gaskiya ya mun daɗi, don Abbun ku da sauran ƴan uwan ku duk suna so, ni kaɗai ne bai dame ni ba, amma daga wannan naji ina so, gaskiya ya yi daɗi, Allah ya miki albarka”.
ta faɗa tana duba na.
Bansan lokacin da nayi tafi ba tsabar jin daɗi, kallon Dr nayi amma shi ko alaman yabawa ban ga ya yi ba, turo baki na nayi gaba kaman zanyi mishi tambayan, amma sanin yanzu zai kushe kawai sai na fasa.
Dariya Amal tayi sannan ta ajiye spoon ɗin ta ta dubi Dr,
“Dr kai ka ɗai fa Hummy ta ke jira taji ka yaba mata, don ni ko na yaba ko kada na yaba ba zai burge ta ba”.
ta faɗa tana ƙunshe dariyan ta.
Ko ɗago kan shi baiyi ba, naji yana cewa, “To ni ai kunyar Abbu ne ya saka ni cin abincin, tun daga ƙamshin girkin har ɗanɗanon shi bai yi mun ba, kawai babu yadda na iya ne, amma girki kaman ba a saka maggi ba”.
Bansan lokacin da kuka ya zo mun ba da ƙarfin gaske, tashi nayi tsaye ina kallon Abbu nace,
“Abbu kaji shi ko? Wallahi bai taɓa cewa nayi abu dai-dai ba, kuma ko wani irin kwalliya nayi baya cewa nayi kyau, kuma gashi a gaban ka yace abinci na ko maggi babu, don Allah Abbu kace yace ya yi daɗi, idan ba haka ba wallahi ihu zan tayi”.
na faɗa ina ƙara sautin kuka na.
Banda dariyan mugunta babu abinda Amal ta keyi, kaman bada ga gadon asibiti ta taso da ƙyar ba, amma ganta yadda ta ke dariyan mugun ta.
“Ummi kinga Amal ko”.
Na sake faɗa ina kukan.
“Allah Amal zan saɓa miki idan bakiyi shiru ba, ke koda wasa za kiyi quater wannan girkin ne? Ke banda indomie me ki ka iya dafawa”.
Cewar Ummi da ta ke hararan Amal.
Abbu ne ya dubi Dr Hussain yace, “haba Dr, yanzu tsakani da Allah haka zanta fi na barka da ƴaƴan amanan kana saka mun su kuka? Yanzu fa akan ido na ƴata tayi girki mai daɗin gaske amma ka ƙi yabawa? Ashe kuma dama haka ka ke kushe mata girkin ta, yau ne Allah ya kama ka ka yi a gaba na? Sannan mai kyau kaman tauraruwa amma baka taɓa yaba kyaun ta ba? Ka gaya mun akwai sauran wata mai kyau da ka taɓa gani sama da ita?”
Ɗago kai ya yi yana duba na kaman yaga kashi, sannan ya dubi Abbu yace,
“Abbu bana ganin kyaun yarinyar nan, kuma ni girkin ta tayar mun zuciya ya keyi, kawai saboda kaine na ci, amma yarinyar nan jagwalgwale kawai ta keyi mutane suna ci basu sani ba”.
ya faɗa yana ajiye spoon ɗin hannun shi.
Ban jira mai za ace mishi ba na juya da gudu nayi ɗaki na, ina kuka kaman ance yau ba’a ga iyaye na ba.



