Home Labarai Sheikh Jingir: ’Yan Najeriya da su mayar da hankali kan manufofi, ƙwarewar...

Sheikh Jingir: ’Yan Najeriya da su mayar da hankali kan manufofi, ƙwarewar ’yan takara maimakon bambancin addini—Fani Kayode

15
0

Fani-Kayode ya soki Sheikh Jingir bisa kalaman da ya yi kan tikitin Musulum-Musulum

Tsohon Ministan Sufuri, Femi Fani-Kayode, ya bayyana kalaman malamin addinin Musulunci, Sheikh Yahya Jingir, na neman a ci gaba da amfani da tikitin shugaban ƙasa na Musulmi da Musulmi a zaɓen 2027 a matsayin kalaman da za su iya tayar da hankali.

Jingir ya yi kira ga Musulmi da su goyi bayan tikitin Musulmi da Musulmi, yana mai cewa ba zai sauya matsayinsa kan hakan ba. Ya kuma bukaci Musulmi su mallaki katin zaɓe domin shiga zaɓen 2027.

Sai dai Fani-Kayode ya ce irin wannan magana “tana da matuƙar tayar da hankali”, yana gargadin cewa kaifin kishin addini na iya jefa ƙasar cikin hatsari.

Ya bayyana Najeriya a matsayin ƙasa mai bin tsarin zamani kuma mai ɗauke da Musulmi da Kiristoci, yana mai cewa bai kamata addini ya zama abin raba kan ’yan ƙasa ba.

Fani-Kayode ya ce goyon bayansa ga tikitin Musulmi da Musulmi a 2027 ya samo asali ne daga cancanta, ƙwarewa, halayya da ƙarfin ’yan takarar, ba wai saboda addininsu ba.

Ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su mayar da hankali kan manufofi, ƙwarewar ’yan takara da abubuwan da za su amfani ƙasa, maimakon bambancin addini.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here