Mi ya sa ba a ga sunan Sheikh Jingir da Rarara ba a kwamitin yakin neman zaben Tinubu ba?
Jam’iyyar APC ta nada Sheikh Halliru Maraya daga Kaduna da Sheikh Aminu Abu Ammar a matsayin wasu daga cikin malaman da za su tallata takarar Tinubu a tskanain Musulmai a kwamitin yakin neman zaben Tinubu, yayin da a bangaren ‘yan fim aka samu Ali Nuhu da Mansurah Isah a matsayin wadanda za su tallata Tinubu a kwamitin.
Sai dai rashin ganin babban malamin Islama Sheikh Jingir wanda ya yi suna wajen tallata takarar Tinubu ta Muslim-Muslim a jerin malaman Islama da za su tallata Tinubu da fitaccen mawakin APC Rarara a cikin kwamitin yakin enman zaben Tinubu ya haifar da muhawara, inda wasu ke mamakin rashin ganin sunayensu yayin da wasu ke cewa za a iya sanya su daga baya ko kuma aikinsu bai zama dole sai an sanya su a cikin kwamitin ba. Ya kuke kallon wannan lamarin?






