Home Rahoto Gwamnatin Kebbi ta ƙirƙiri wata sabuwar Gunduma a jihar

Gwamnatin Kebbi ta ƙirƙiri wata sabuwar Gunduma a jihar

16
0

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya amince da ƙirƙirar sabuwar Gundumar Ummu a Ƙaramar Hukumar Zuru ta jihar.

Sabuwar gundumar za ta kasance ƙarƙashin Gundumar Rafin Zuru, kamar yadda Kwamishinan Ƙananan Hukumomi da Harkokin Masarautu na Jihar Kebbi, Alhaji Garba Umar Dutsinmari, ya bayyana.

Kwamishinan ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya sanya wa hannu tare da rabawa manema labarai a Birnin Kebbi ranar Juma’a, 11 ga Satumba, 2026.

Sanarwar ta ce, Gwamna Nasir Idris ya amince da naɗa Alhaji Aliyu Ibrahim Gujiya a matsayin Hakimin Gundumar Ummu.

A cewar Kwamishinan, an fitar da Gundumar Ummu ne daga cikin Gundumar Rafin Zuru, kuma ta ƙunshi ƙauyuka guda takwas.

Ƙauyukan da sabuwar gundumar ta ƙunsa sun haɗa da Paso, Sondoro, Denkre, Akwanchi, D’hava wanda aka fi sani da Hato, Daklo, Ummu Gari, da kuma Bedi.

Kwamishinan ya bayyana cewa ƙirƙirar sabuwar gundumar da naɗa hakimin sun yi daidai da tanadin Dokar Ƙananan Hukumomin Jihar Kebbi ta shekarar 2008, musamman Sashe na 10, ƙananan sassan A da B.

Ya ce waɗannan tanade-tanade na doka sun bai wa gwamnati ikon ƙirƙirar gundumomi tare da naɗa shugabannin gargajiya da za su jagorance su.

Da yake magana kan sabon muƙamin, Alhaji Garba Umar Dutsinmari ya buƙaci sabon Hakimin Gundumar Ummu, Alhaji Aliyu Ibrahim Gujiya, da ya gudanar da aikinsa bisa gaskiya, riƙon amana, ladabi, da kuma kishin al’umma.

Ya kuma buƙace shi da ya kasance mai bin doka da oda tare da yin aiki tukuru wajen tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban al’ummar da aka damƙa masa.

Kwamishinan ya tabbatar wa sabon hakimin cewa Gwamnatin Jihar Kebbi da ma’aikatar da yake jagoranta za su ci gaba da ba shi goyon baya da haɗin kai wajen gudanar da ayyukansa.

Gwamnatin Jihar Kebbi ta ce ƙirƙirar sabuwar gundumar na daga cikin matakan da take ɗauka domin ƙarfafa hukumomin gargajiya da kuma inganta tsarin gudanar da mulki a matakin ƙasa.

Gwamnatin ta kuma jaddada cewa za ta ci gaba da ɗaukar matakan da za su taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya, haɗin kan al’umma da kuma samun ci gaba mai ɗorewa a faɗin Jihar Kebbi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here