Rahotanni sun nuna cewa ‘yan bindiga masu biyayya ga Isiya Kwashen Garwa sun sake kakaba harajin Naira miliyan 10 ga kowace al’umma a Garin Lamido da Yan Shuni, da ke ƙaramar hukumar Bakori a Katsina State.
Wannan sabon mataki na zuwa ne duk da yarjejeniyoyin sulhu da aka cimma a baya tsakanin hukumomi, masu ruwa da tsaki da kuma ƙungiyar ‘yan bindigar.
Rahotanni sun ce wannan lamarin ya haifar da tsananin fargaba a yankin, inda mazauna da dama suka fara guduwa daga gidajensu domin tsira da rayukansu.






