Zulum na shirin sayar da man fetur ga manoma kan N600

Zulum na shirin sayar da man fetur ga manoma kan N600

Zulum na shirin sayar da man fetur ga manoma kan N600

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya sanar da cewa gwamnatin jihar za ta rage farashin man fetur ga manoma a yankunan da rikicin Boko Haram ya shafa.

Zulum ya sanar da wannan tallafi ne a jiya Juma’a a garin Bama yayin da ya kaddamar da rabon kayan noma ga manoma sama da 5,000 da Boko Haram ta taba korar su daga muhallansu.

A cewar gwamnan, farashin litar man fetur da ake sayarwa tsakanin N1,000 zuwa N1,200 a Maiduguri za a sayar wa manoma kan N600.

Wannan mataki, a cewar sa, na da nufin rage nauyin kudin da ke kan manoman a yankunan da su ka fuskanci lalacewar tattalin arziki da gine-gine sakamakon shekaru na rikici.