Yakamata Gwamnatin Tarayya Ta Janye Tallafin Mai Ta Maida Shi Ga Noma-----Shugaban Manoman Masara

Yakamata Gwamnatin Tarayya Ta Janye Tallafin Mai Ta Maida Shi Ga Noma-----Shugaban Manoman Masara
 

Daga Hussaini  Ibrahim, Gusau

 

 Shugaban kungiyar masu Noman  masara na jihar, Zamfara, watau (MAN)  Alhaji Abdullahi  Kwanda,  yayi kira ga gwamnatin tarayya  da ta cire tallafin man Fetir ta maida shi ga sashen  Noma musamman  takin dan tallafin  abinci yafi mahimmanci akan na man Fetir. 

 
Abdullahi Kwanda ya bayyana haka  ne a lokacin da ya ke tattaunawa  da wakilin  mu a Gusau  babban  birnin  jihar Zamfara. 
 
Nakwada ya kara  da cewa,  bilyoyin nairori  da gwamnati ke badawa wajan dauko man fetir  da gwamnati zata badasu wajan takin zamani lallai da munciyar da afunka baki daya,  arzikin kasar mu zai bunkasa fiye da yadda bamuyi tsammani. dan Taki zai wadata manoma zasu samu taki cikin farashi mai sauki, matasa zasu samu abunyi rani da damuna.  kuma zai rage zaman kashe wando ga matasa kuma zaitaimaka wajan samar da tsaro.  kuma aikin gona rigakafine  ga matasa wajan dogara dakai. Kuma zaisamar da ingantacan dawamamen zaman lafiya. dan idan matasan mu basu da aikinyi, abu mai saukine su fada a harkar da bata dace  da su ba. Inji Shugaban manoman masara na jihar Zamfara. 
 
Ya ya koma kan batun manyan 'yan kasuwa kuma masu sana'ar saida taki Shugaban yayi kira a garesu  da su samar  da kamfanoni sarafa taki a cikin wannan gida Kasa tamu ta yadda babu bukatar sayan takin  zamani na qasashen wake. Dan yanzu haka akwai Kamfanini da keyin takin zani mai inganci a Kasar nan wanda Kananan manoma zasu yi amfani da shi kuma su samu amfanin mai inganci. 
 
Haka kazalikama idan gwamnatin jahohi masu kamfanin taki zasu tada kamfanonin su zasu iya samar da taki ga manoma da zasuyi amfani da shi acikin sassaukan farashi. asamar da abuncin da ba'ayi tsamaniba. 
 
A karshe Abdullahi Kwanda yayi kira musamman ga manoman Masara da kada tsadar taki ta basu tsoro a Noman bana ya kamata suyi amfani da takin gargajiya da kuma takin da ake ayinsa anan kasar mai saukin farashi kuma yana da Inganci  sosai wajan gudanar na noman su. dan yanzu haka akwai shiri na musamman da Uwar Kungiyar ta masu Noman Masara keyi, Karkashin jagoranci Shugaban ta na Kasa, Alhaji Bello Annur, dan sambar wa mambobin kungiyar hanyoyin cigaban noma na zamani.