Tinubu ya kuduri aniyar kawar da 'yan bindiga

Tinubu ya kuduri aniyar kawar da 'yan bindiga
 
Daga Abbakar Aleeyu Anache.
Mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya yi gargadin cewa ba za a amince da kawo cikas ga harkokin tsaro a gwamnatin shugaba Bola Tinubu ba, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya ruwaito.
 
Ya bayyana haka ne a wajen taro da aka yi a Abuja ranar Laraba, inda ya jaddada aniyar shugaban kasar na kawar da ‘yan fashin daji, ‘yan ta’adda, da sauran matsalolin tsaro.
 
A cewar Ribadu, manyan tsare-tsare na gwamnati sun kai ga kashe daruruwan ‘yan bindiga a kullum, wanda ya tilastawa da dama yin gudun hijira zuwa kasar Chadi.
Ya ce shugaba Tinubu ba zai sassautawa duk wani mai kawo cikas ga tsarin kasa.