Tambuwal Ya Rantsar Da Manyan Alkalan Babbar Kotu 5 Da Khadi 2 A Sakkwato

Tambuwal Ya Rantsar Da Manyan Alkalan Babbar Kotu 5 Da Khadi 2 A Sakkwato

 

Gwamnan Jihar Sakkwato Aminu Waziri Tambuwal  ya rantsar da Manyan Alkalan  Babar Kotun Jiha  5 da Khadi biyu a zauren fadar gwamnatin jiha a wannan jumu'ar.

Tambuwal ya rantsar da su ne kamar yadda doka ta ba shi dama domin aiwatar da aiyukkan kotuna daban-daban a fanin shari'a a jihar.

Alkan da aka rantsar hudu maza da mace daya  Sanusi Shehi Esq da Prof. Muawiya Dahiru Mahmud Esq da Abubakar Abubakar Zaki Esq da  Mohammed Aliyu Sambo Esq da  Maryam Muhammad Esq.
 

 Bayan nan kuma ya rantsar da Khadi su biyu  Buhari Yahaya da  Dakta  Umar Jibril Kebbe.