Home Uncategorized Sojoji Sun Yi Kofar Rago ga Bello Turji, Ana Kokarin Cafke Shi 

Sojoji Sun Yi Kofar Rago ga Bello Turji, Ana Kokarin Cafke Shi 

7
0

Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya sha alwashin kama babban dan ta’adda, Bello Turji, da ya shahara da ta’addanci a Sokoto, Zamfara, da Kebbi. Janar Musa ya ce kama Turji abu ne da lokaci kawai ya rage, domin sojoji na ci gaba da gudanar da tsare-tsare wajen ganin hakan.
Da yake magana a wani shiri na musamman da aka watsa a tashar Channels Television, Janar Musa ya ce ‘yan ta’adda da dama sun mika wuya a Najeriya. 
Babban Hafsan Tsaro, Janar Musa, ya ce an yi nasarar kakkabe dukkan kwamandojin Bello Turji da suka rika taimaka masa wajen gudanar da ta’addanci a Arewa maso Yamma. “Tun da ya fahimci cewa muna bibiyarsa, sai ya fara buya amma muna ci gaba da gudanar da aiki a kansa. Muna kama duk wanda ke kusa da shi, kuma mun kashe kwamandojinsa.” – Janar Christopher Musa Sojoji na gudanar da hare-hare kan duk masu bayar da goyon baya ga Turji a jihohin Sokoto, Zamfara, da Kebbi, domin tabbatar da cewa ya rasa mafaka ko taimako daga kowane bangare. 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here