Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Safar 

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Safar 

 

Mai Martaba Sarkin musulmi Alhaji Sa'ad Abubakar ya ba da umarni ga al'ummar musul,mi da su fara duban watan Safar daga gobe Lahadi 29 ga Muharram dai da 4 ga Agustan 2024.

Sarkin musulmi ya ba da sanarwar ne a wata takarda da Wazirin Sakkwato Farfesa Sambo Wali Junaid ya sanyawa hannu ya ce an nemi mutane su dubi watan Safar a Lahadi, duk wanda ya gani ya kai rahoto a wurin hakimi ko uban kasar da ke kusa da shi domin sanar da mai martaba Sarkin musulmi.
Ya roki Allah ya taimake su ga aikin addini da suke yi.