Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kaduna, Muhammad Rabiu, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan zargin yunkurin kashe Sanata Usman Lawal (PDP Kaduna-Central).
Umurnin binciken na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Mansir Hassan, ya fitar ranar Alhamis a Kaduna.
Hassan ya ce, “’Yan sanda ba su san da yunkurin kashe Sanata Usman Lawal ba.
“An jawo hankalin hukumar ne ga wani buga a shafin Facebook na Sanata Lawal Usman.
Ya yi ikirarin cewa ya tsallake rijiya da baya a wani yunkurin kashe shi da wasu ‘yan daba suka yi a wani wurin da har yanzu ba a san ko su waye ba a Kaduna ta Arewa a ranar Laraba, kuma ba a bayar da lokacin faruwar lamarin ba.
Daga Abbakar Aleeyu Anache





