Sanata Lamido ya yi Ta'aziyar rasuwar tsohon mataimakin gwamnan Sakkwato

Sanata Lamido ya yi Ta'aziyar rasuwar tsohon mataimakin gwamnan Sakkwato

Sanata Ibrahim Lamido ya yi ta'aziyar rasuwar tsohon mataimakin gwamnan Sakkwato Alhaji Ahmad Muhammad Gusau wanda ya rasu a jiya Jumu'a, bayan fama da doguwar jinya.
Sanata Lamido a bayanin da ya fitar da kansa ya mika sakon ta'aziyar ga iyalai da masoya da mutanen Sakkwato baki daya.
Sanata ya bayyana marigayin a lokacin rayuwarsa mutum ne karimci da sakin fuska da son gaskiya a harkokinsa, ya roki Allah ya gafarta masa.
Ibrahim Lamido ya ce marigayi ya bar giɓi mai wuyar cikewa kan haka ya roki iyalai da su jure kan rashin da aka yi a jiha da kasa baki daya.