Ruwan Sama Sun Yi  Ambaliya a Garuruwan Kebbi

Ruwan Sama Sun Yi  Ambaliya a Garuruwan Kebbi
i
Ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka fara tun ranar Alhamis da daddare har zuwa yammacin ranar Juma'a ya kai ga rugujewar wata gada a karamar hukumar Maiyama ta jihar Kebbi.
Rahotanni daga yankin na cewa, gadar da ta hada, Mayalo, Sambawa, Gumbin-Kure, Uguwar Shuaibu, da Gandiji, ta ruguje ne a ranar Juma’a sakamakon ruwan sama da ake ci gaba da yi.
An samu Ambaliya wasu garuruwan jihar Kebbi har yanzu ba a kai ga sanin hasarar da aka yi ba.
 Abbakar Aleeyu Anache