NLC Ta Lissafa Sharudda Shida Kafin  Janye Yajin Aiki

 NLC Ta Lissafa Sharudda Shida Kafin  Janye Yajin Aiki


Shuwagabannin kungiyar kwadago ta kasa NLC, sun bayyana wasu sharudda shida da ya zama wajibi a cika su kafin kungiyoyin kwadago a kasar su janye yajin aikin da suke yi. 
Sun jera sharuddan shida a cikin wata sanarwa da suka fitar a shafin kungiyar na X (wanda aka fi sani da Twitter) ranar Talata. 
Kungiyar ta NLC ta ce, da farko dole ne a kama Chinasa Nwaneri, mai ba Gwamnan Imo shawara, da ake zargin shi ne ya jagoranci harin da aka kaiwa shugaban NLC da sauran ma’aikata a jihar, tare da kai shi gaban kotu. 
Kungiyar ta kuma ce a kama dukkan jami’an ‘yan sanda da kuma ‘yan daba da ke da hannu a harin da aka kai wa shugaban kungiyar, a gurfanar da su gaban kuliya tare da korarsu daga aiki. Haka kuma, ta bukaci a kama, gurfanarwa tare da korar babban jami’in tsaro a gidan gwamnatin jihar Imo, wanda aka fi sani da SP Shaba. “Ya jagoranta tare da bayar da mafaka ga ‘yan daba don muzgunawa ma’aikata a jihar Imo,” NLC ta yi zargin. 
Wani sharadi da kungiyar kwadago ta bayar shi ne kamawa, hukuntawa da kuma korar wani kwamandan ‘yan sandan da ba a bayyana sunansa ba, wanda ta ce shi ne ya ba da damar cin zarafin shugaban NLC da sauran ma’aikata a jihar. Sharadi na shida don kawo zaman lafiya shi ne cewa, dole ne a binciki tsohon kwamishinan ‘yan sandan jihar Imo, Ahmed Barde, tare da gurfanar da shi a gaban kuliya bisa zarginsa da hannu wajen cin zarafin shugaban NLC. “Bukatunmu masu sauki ne. Muna neman adalci". - Cewar NLC 
Kamar yadda Legit Hausa ta ruwaito, kungiyoyin kwadago na Najeriya NLC da TUC, sun umurci mambobinsu da su fara yajin aiki a fadin kasar, sakamakon harin da aka kaiwa shugaban NLC, Joe Ajaero.