Mutum Uku Sun Rasa Ransu Sanadiyar Ruftawar Kasa a Keffi

Mutum Uku Sun Rasa Ransu Sanadiyar Ruftawar Kasa a Keffi

Mutane uku sun rasu yayin da wasu kuma suka jikkata a wani hadarin zaftarewar kasa da ya faru a yankin Keffi na jihar Nasarawa ta Najeriya.

Shugaban Karamar Hukumar ta Keffi, Muhammad Baba Shehu ya tabbatar da hakan a wata hira da BBC.

Lamarin dai ya faru ne da yammacin ranar Talata a lokacin da mutanen ke hakar yashi a wani wurin ɗibar yashi da ke unguwar Ayaba.

Nasarrawa na daga cikin jihohin Najeriya waɗanda ke da arziƙin albarkatun ƙasa.

Haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba abu ne da ya zama ruwan dare a Najeriya, lamarin da a lokuta da dama kan haifar da mutuwar mutane saboda rashin ɗaukar matakan kariya da suka kamata.