Mi Ya Hana Walin Sakkwato  Sanya Tallar Taya Sarkin Musulmi Murnar Zagayowar Ranar Haihuwarsa Kamar Yadda Ya Saba?

Mi Ya Hana Walin Sakkwato  Sanya Tallar Taya Sarkin Musulmi Murnar Zagayowar Ranar Haihuwarsa Kamar Yadda Ya Saba?

Mataimakin Gwamnan jihar Sakkwato Honarabul Manir  Muhammad Dan’iya Walin Sakkwato tun sanda ya zama mataimaki gwamna, a duk shekara yakan biya kudin shafi daya mai kala a jaridar Daily Trust ya taya Sarkin Musulmi murnar zagayowar ranar haihuwarsa, kan tsawon shekarun da ya yi a duniya lafiya lau a cikin jagorantar jama’a  da yi masa fatan alheri.

Kamar yadda ya yake yi  sama da shekara biyar wannan ya zama wata al’ada ta yi wa Sarkin Musulmi kara a wannan haujin, in da mutane musamman masana da masu bibiyar harkokin yau da kullum ke yin sam barka da wannan karar dake fitowa a wurin mutum mai daraja ta biyu, a jihar da Sarkin Musulmi ke jagorantar al’ummar Nijeriya gaba daya.

Wannan abin da yake masa kwarai yake kara daga kima da darajar masarauta a idon Duniya ganin yanda ake yi wa Sarkin Musulmi Sadaukarwa, hakan na nuna yanda yake zaman lafiya da masu mulkin jihar wanda abin so ne ga tafiyar sarauta kowace iri.

A gefen Sakkwatawa masu bibiyar lamurran yau da kullum  wannan karimci  yana share hawayensu ganin yanda zuma ke yi wa kanta zaki, kenan masu mulki a Sakkwato za su yi kowace sadaukarwa kan Sarkinsu, wannan sauke faralin nasu yana janyo wasu a jihohin Nijeriya biyo bayan su don su yi mustahabbi ganin ba wanda yake jiransu Sarki yana da gata a jiharsa.

Kwatsam wannan shekarar mai aiki ya dakatar da aikinsa MANAGARCIYA ta yi rabon ido tare da ba da cigiyar taya murnar Walin Sakkwato ga Sarkin Musulmi ta cika shekara  66 a jaridar Daily Trst ba a samu wanda ya ci karo da ita ba, abin da ke nuna a wannan shekarar kam an tafi hutu, sai dai abin ba a sani ba hutun na wuccin gadi ne ko na har abada ne?.

Don sanin abin da ya hana sanya wannan tallar a wannan shekarar duk kokarin jin ta bakin Walin ko wani na kusa da shi lamarin ya faskara domin ba a samu wata nasara ba.