Home Rahoto Ma’aikatan Zakka 8 sun yi hatsarin mota a hanyar su ta zuwa...

Ma’aikatan Zakka 8 sun yi hatsarin mota a hanyar su ta zuwa Sokoto

19
0

Ma’aikatan Hukumar Zakka da Waƙafi ta Jihar Katsina takwas sun yi hatsarin mota a hanyarsu ta zuwa Jihar Sokoto.

Arewa Updates ta rawaito cewa, wannan na cikin sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Hukumar, Malam Husain Kabir Yar’adua, ya fitar.

Ya ce, ma’aikatan sun gamu da hatsarin a tsakanin Yankara da Tsafe yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa Sokoto domin halartar taron Bankin Raya Musulunci na Duniya IsDB.

Hukumar ta bayyana cewa mutum ɗaya ya samu karaya, yayin da sauran suka samu raunuka daban-daban, inda aka dawo da su Katsina kuma suke samun kulawar likitoci.

Hukumar ta bukaci al’ummar Musulmi da sauran jama’a su yi wa ma’aikatan addu’ar samun sauƙi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here