Kungiyar Malaman Jami'o'i, ASUU ta tsunduma yajin aiki
Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Neja Delta (NDU), mallakin gwamnatin Jihar Bayelsa ta tsunduma yajin aikin sai baba-ta-gani, sakamakon rashin cika yarjejeniyoyin da aka cimma da kungiyar a baya.
ASUU ta sanar da matakin ne a yau Talata bayan wani taro da ta gudanar a sakatariyar ta da ke Amassoma.
Sai dai kuma ana sa ran yajin aikin zai kawo cikas ga harkokin ilimi a jami'ar, lamarin da ya jefa dalibai da masu ruwa da tsaki cikin rashin tabbas.
managarciya