Kokarin da A.A Gumbi Ke Yi Na Kawar Da Bangar Siyasa Abu Ne Mai Kyau----- Haruna Shehu

Ya ce a halin da ake ciki yanzuma wasu da dama suna nan suna karbar horo a jihar zamfara a halin yanzu,  ya kara da cewa ya dace masu hannu da shuni su rika daukar darasi daga gareshi . Da yake amsa tambayar wakilinmu   daya daga cikin matasan da suka amfana da samun wannan tallafi na  aiki, duk da cewa yace yana bukatar a sakaya sunan sa ,ya ce babu abinda zai ce sai godiya sakamakon yadda a baya  yaketa gararanba, wajan neman aiki amma abin yaci tura, yace amma ta hanyar wannan bawan Allah "Na sami aikin " in ji shi

Kokarin da A.A Gumbi Ke Yi Na Kawar Da Bangar Siyasa Abu Ne Mai Kyau----- Haruna Shehu
A A Gumbi

 

Daga Aminu Abdullahi Gusau.

 

An bayyana Alhaji  Abdullahi Abubakar A .A Gumbi a matsayin jagora na gari maihalin 'yan mazan jiya.

 
Hakan ya  fitone daga bakin shugaban kungiyar neman hadin kan matasa ta kasa watau United Nigeria youth a turance, kwamred Haruna Shehu a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Sokoto. 
 
Ya kara da cewa sakamakon kokarin da Alhaji Abdullahi yake yi  na ganin sai ya kauda bangar siyasa a tsakanin matasa ta hanyar Samar musu da aikin yi, hakan ya sanya jama'a da dama suka rika jinjina masa.
 
Haruna Shehu ya ce Alhaji   Abdullahi ya samarwa matasa da dama aikin yi musamman aikin jami'an  immigration, watau masu kula da harkar shigi da fice ta kasa, da aikin 'yansanda da sauran aikin kaki da dai sauransu.
 
Ya ce a halin da ake ciki yanzuma wasu da dama suna nan suna karbar horo a jihar zamfara a halin yanzu,  ya kara da cewa ya dace masu hannu da shuni su rika daukar darasi daga gareshi .
 
Da yake amsa tambayar wakilinmu   daya daga cikin matasan da suka amfana da samun wannan tallafi na  aiki, duk da cewa yace yana bukatar a sakaya sunan sa ,ya ce babu abinda zai ce sai godiya sakamakon yadda a baya  yaketa gararanba, wajan neman aiki amma abin yaci tura, yace amma ta hanyar wannan bawan Allah "Na sami aikin " in ji shi.
 
Sai dai Haruna Shehu bai  tsaya nan ba in da ya bayyana cewa mafi yawan matasan arewa suna rasa aikinyi ne saka makon rashin masu tallafawa, ya ce  da ana samun jagorori irin Alhaji Abdullahi Abubakar da wuta ta mutu, saboda mafiya yawan matasan Arewacin kasan nan ba zasu shiga bangar siyasa ba.