Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn domin inganta kiwon lafiya
Join our subscribers list to get the latest news, updates and special offers directly in your inbox
Wannan shiri na da nufin bunƙasa fannin kiwon lafiya da ingancinsa, da kuma cike giɓin da ake da shi a ɓangaren a Jihar Sakkwato, a cewar AfDB ta bayyana a cikin wata sanarwa ranar Juma’a.
Rahotanni na nuni da cewa, yaro ɗaya cikin kowane yara 20 ne akale yi wa allurar rigakafi cikakke a Jihar Sakkwato a, a yayin da adadin mutuwar jarirai ya kai 104 daga cikin 1,000 a Jihar.
Ƙasa da kashi 14 cikin 100 na cibiyoyin lafiya a jihar ne suke da kayan aiki masu aiki, kuma likita ɗaya ne kawai ke kula da mutum 8,285, wanda ya gaza abin da Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayar na likita 1 ga 1,000 mutum
Kuɗaɗen da bankin ya ware za su tallafa wa samar kayan aikin kula da lafiya masu inganci a matakai uku na kula da lafiya a Jihar Sakkwato.
Wannan ya haɗa da gina sabon asibitin koyarwa mai gado 1,000, da manyan asibitoci na yankuna uku masu jimillar gadaje 450, da kuma cibiyoyin kiwon lafiya guda shida da aka tsara a domin kuka da al’ummomin karkara.
Aikin ya kuma haɗa da gyaran cibiyoyin horar da ma’aikatan lafiya da ƙirƙirar sabon ma’ajiyar magunguna ta zamani.
Darakta-Janar na Ofishin AfDB a Najeriya, Abdul Kamara, ya ce, “Wannan rancen na nuna yadda muke jajircewa wajen aiki tare da gwamnati don magance giɓin kayan kiwon lafiya a Najeriya, tare da gina cibiyoyin kula da lafiya masu ƙarfi da suka dace da tsari na yanayi.
“Ta hanyar ƙarfafa kayan aikin lafiya a Jihar Sakkwato, muna gina fata da hanyoyin samun kyakkyawan sakamako ga miliyoyin ’yan Najeriya.”
managarciya Oct 30, 2021 12 177
managarciya Feb 3, 2025 3 118
Maryamah Dec 14, 2021 2 96
managarciya Jun 24, 2023 5 88
Maryamah Dec 16, 2021 10 81
managarciya Nov 13, 2023 0 549
managarciya Nov 12, 2023 0 344
managarciya Nov 12, 2023 0 334
managarciya Nov 12, 2023 0 415
managarciya Nov 11, 2023 1 701
managarciya Aug 15, 2021 1 1047
managarciya Dec 4, 2025 0 25
managarciya Dec 3, 2021 1 582
Shugabar gidauniyar Zarah and Arthur, Hajiya Zarah I. Abdullahi tayi kiran a lokacin...