Jam'iyar APC Ta ce Yin zanga zangar adawa ga Gwamnatin Tinubu zai kawo illa ga ci gaban kasa

Jam'iyar APC Ta ce Yin zanga zangar adawa ga Gwamnatin Tinubu zai kawo illa ga ci gaban kasa

Jam'iyar APC shiyyar Arewa ta tsakiya ta yi gargadi kan shirin da wasu kungiyoyi da daidaikun mutane keyi  na shirya zanga-zangar adawa da gwamnatin shugaba Bola Tinubu a fadin kasar.

Taron ya ce irin wannan matakin ba za ta yi tasiri ba zai yi kuma illa ga ci gaban kasar a halin yanzu, inda ta yi kira ga masu shirya Zanga zangar da su sake tunani, su kuma ja da baya.

Shugsban muryar yan jamiyyar APC a yankin, Saleh Mandung Zazzaga, a taron manema labarai a Jos a yau Litinin ya yi kira ga masu shirya zan-zangar da su yi duba na tsanaki a kan yanayin da kasar ke ciki kafin su yanke hukunci.

A cewar sa, Tinubu na iya kokarin san a wajen seta Nijeriya, inda ya yi kira gay an kasar da su mara masa baya a maimakon yi wa gwamnatinsa zagon-kasa da sunan zanga-zanga.