Gwamnonin PDP za su kai matsaya kan yankin da zai fitar da shugaban kasa

Gwamnonin jam'iyar PDP a Nijeriya a yau Laraba a Abuja za su cimma matsaya kan yankunan da za a fitar da shugabannin jam'iya da za su jagaoranci jam'iyar ta adawa.

Gwamnonin PDP za su kai matsaya kan yankin da zai fitar da shugaban kasa
Gwamnonin PDP za su kai matsaya kan yankin da zai fitar da shugaban kasa

Gwamnonin jam'iyar PDP a Nijeriya a yau Laraba a Abuja za su cimma matsaya kan yankunan da za a fitar da shugabannin jam'iya da za su jagaoranci jam'iyar ta adawa.

Daily Trust ta samu bayani maganar karba-karbar tana cikin abin da ya tsayar da kwamitocin mutum 279 da za su gudanar da babban taron kasa na jam'iyar karkashin jagorancin gwamnan Adamawa Umaru Ahmadu Fintiri.

A zaman majalisar zartarwar jam'iyar karo 94 PDP ta kafa kwamitin da zai raba mukaman a kowane yanki na Nijeriya karkashin kulawar Gwamnan Ifeanyi Ugwuanyi kafin babban taron 30 ga Okotoba 2021.
Zaman da kwamitin ya yi a satin da ya gabata a Enugu sun aminta da kudu ce za ta kawo shugaban jam'iya, kwamitin zai yiwa gwamnoni bayanin matsayarsu a yau.

Taron zaman na kungiyar Gwamnonin PDP karkashin jagorancin Gwamnan Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ana sa ran su tattauna wasu muhimman bayanai game da harkar shugabanci.