Cire Sarkin Musulmi: dokar akwai bukatar a yi takatsantsan---Dan Majalisar jiha

Cire Sarkin Musulmi: dokar akwai bukatar a yi takatsantsan---Dan Majalisar jiha

  Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Isa Honarabul Habibu Halilu Modachi ya ce kudirin dokar da aka kawo a gaban majalisa  baya da wata alaka da cire sarkin musulmi amma dai wasu sassan na dokar akwai bukatar a yi takatsantsan sosai kan su domin ganin abin da ke faruwa a Kano, kan haka na gayawa majalisa da ta yi abin da ya dace domin zaman lafiyar jihar Sakkwato.

"tun sanda Sarkin musulmi yake nadawa ba a taba samun wata hatsaniya a kai ba, saboda mi za a sauya tsarin, mutane su kwantar da hankalinsu muna tare da su kuma za a yi abin da ya dace a majalisa.

"Babu maganar cire Sarkin musulmi a majalisa abin da ke nan maganar sarakuna ce da sarkin musulmi ke nadawa yanzu an kawo  cewa gwamna ne zai a amincewa Sarkin musulmi, in ka duba a matsayin su na uwaye wannan dan aikin ne dai suke yi, in an ce babu wannan ka ga kamar an cire su ne." 

Wasu mutane a jiha na ganin dacewar jingine dokar duk da gwamnatin jiha na ganin da cewar yi wa dokar gyran fuska.