Buhari ya sallami ministocinsa biyu

Buhari ya sallami ministocinsa biyu

Buhari ya sallami ministocinsa biyu

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya sallami ministocinsa guda biyu  ministan Gona Muhammad Sabo Nanono da ministan Wuta Mamman Saleh

Femi Adesina, mai magana da yawun shugaban ƙasa ne ya sanar da manema labarai a fadar shugaban ƙasa a yau Laraba. 

Ya ce an maye madadinsu da ministan Muhali Mohammad Mahmoud Abubakar da ƙaramin ministan aiyukka da gidaje Abubakar Aliyu

A lokacin buga wannan labarin ba su bayar da dalilin sauke ministocinsa.