Abin Da Ya Sa Zaben Tambuwal, Wamakko Da Gwanda Bai Kammala Ba---INEC

Abin Da Ya Sa Zaben Tambuwal, Wamakko Da Gwanda Bai Kammala Ba---INEC

Gwamnan jihar Sakkwato Aminu Waziri Tambuwal da Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko da Gwanda Gobir da  sauran ‘yan takara 10 da suka  nemi kujeru a majalisar  wakilai ta tarayyar Nijeriya  zabensu bai kammala ba kaamar yada hukumar zabe ta kasa reshen jihar Sakkwato ta sanar a cibiyoyin tattara sakamakon zabe daban-daban dake cikin jiha.

Gwamnan Sakkwato da yake neman kujerar Sanata a yankin  kudancin Sakkwato cikin jam'iyar PDP shi ke kan gaba kafin a aiyana zabensa matsayin wanda bai kammala ba.

Farfesa Shehu Usman Gobir a sakamakon zaben da ya fitar Tambuwal na kan gaban Sanata Ibrahim Danbaba Dambuwa da kuri’a dubu 7,859 in da mutum  83,036  ba su yi zabe ba don haka za a ba su dama su yi zabe.

Sanata Aliyu Wamakko da yake neman sake komawa Sanata da zai wakilci yankin Sakkwato ta Arewa a jam’iyar APC shi ma zabensa bai kammala ba.

Farfesa Ibrahim Magawata a sakamakon da ya bayyana Sanata Wamakko na gaban Mataimakin Gwamnan Sakkwato Honarabul Manir Dan’iya  da kuri’a dubu 11,732, mutum dubu 121, 010 ne ba su yi zabe ba don haka za a ba su dama kafin a aiyana wanda ya yi nasara.  

Honarabul Shu’aibu Gwanda Gobir ne gaban  Honarabul Ibrahim Lamido dake neman kujerar Sakkwato ta gabas  jami'in tattara zabe ya aiyana zaben su bai kammala ba.

Farfesa Abubakar  Abdullahi  Bagudo a lokacin da ya kammala tattara sakamakon zaben gabascin Sakkwato ya sanar da cewa jam'iyar PDP ce kan gaba a zaben Sanata da kuri'a 2551, yawan kuri'un da ba a yi zabe ba sun kai  dubu 67, 602, a tsarin doka zaben bai kammala ba sai an yi wa wadan nan mutanen zabe.

 A cikin kujerar 'yan majalisar wakillai guda 11, daya ce kawai wadda ake wakiltar kananan hukumomin Yabo da Shagari ta kammala in da jam'iyar PDP ta samu nasara aka kayar da wanda ke sama na jam'iyar APC.