Home Labarai Ana zargin wasu ma’aikatan jinya da sakaci a mutuwar yara biyu a...

Ana zargin wasu ma’aikatan jinya da sakaci a mutuwar yara biyu a Kebbi

10
0

An kama wasu ma’aikatan jinya biyu bisa zargin hannu a mutuwar kananan yara mata biyu a asibitin gwamnati da ke Zuru, bayan rahotanni sun nuna yiwuwar kuskuren bada magani.

Rahotanni sun ce yaran, masu shekaru shida da uku, sun rasu ne a ranar 18 ga watan Maris bayan an yi zargin sakacin da ya shafi allurar da aka ba su yayin jinya a asibitin.

Jami’an tsaro sun tsare wadanda ake zargi a Birnin Kebbi, inda ake ci gaba da bincike domin gano hakikanin abin da ya haddasa mutuwar yaran.

Jaridar Daily Trust ta ambato gwamnatin jihar Kebbi, ta kafa kwamitin bincike mai mambobi tara karkashin jagorancin kwamishinan yada labarai da al’adu, Alhaji Yakubu Ahmed, domin zurfafa bincike kan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here