'Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Uku da Suka Kai Hari a Kasuwa
Ƴan bindiga sun kashe mutum aƙalla uku yayin da wasu da dama suka samu raunuka bayan wani hari da suka kai a wata kasuwa a garin Tsafe, a karamar hukumar Tsafe na jihar Zamfara.
Wani ganau ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi wa kasuwar dirar mikiya ne da misalin karfe 11 na safiyar yau Lahadi inda suka buɗe wuta kan ‘yan kasuwar.
Kakakin ‘yan sandan jihar ta Zamfara, ASP Yazid Abubakar, ya tabbatar wa gidan talabijin na Channels kai harin, inda ya ce kawo yanzu ba a tantance waɗanda harin ya shafa ba.
Abubakar ya ce an tura sojoji da ‘yan sanda zuwa wajen da lamarin ya faru domin fatattakar ‘yan bindigar da kuma dawo da zaman lafiya a yankin.
Mazauna garin na Tsafe sun ce dakarun Hadarin Daji da aka tura zuwa yankin sun fafata da ƴan bindigar tare da tilasta musu tserewa zuwa cikin daji.
managarciya