Tsige Sarkin Musulmi: Mataimakin Shugaban Kasa Ya Gargadi Gwamnan Sakkwato
Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima, ya gargadi Gwamnan Jihar Sakkwato kan yunkurinsa na tsige Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar.
Shettima ya bayyana cewa darajar kujerar Sarkin Musulmi ta wuce iya Jihar Sakkwato, don haka ba abar was ba ce, kuma wajibi ne a ba shi kowace irin kariya da girmamawa.
Shettima ya bayyana haka ne a yayin da ake rade-radin Gwamnan Sakkwato Ahmad Aliyu na shirin tube rawanin Sarkin Musulmi.
“Sakona ga Mataimakin Gwamnan Sakkwato (wanda ke wakiltar gwamnansa a nan) mai sauki ne: hakika Sultan na Sakkwato a karkashin Jihar Sakkwato yake, amma tabbas darajarsa ta wuce iya nan.
“Sarkin Musulmi wani bango ne da dukkanmu a wannan kasar ke bukatar mu mutunta tare da ba shi kariya da goyon baya mu kuma adana,” in ji mataimakin shugaban kasar.
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a taron tsaro da zaman lafiya na yankin Arewa maso Yamma a ranar Litinin a Kastina.
Mataimakin Gwamnan Sakkwato ne ya wakilci Gwamna Ahmad Aliyu a taron.
Aminiya ta ruwaito Kungiyar Kare Hakkokin Musulmi (MURIC) ta zargi Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmad Aliyu da yunkurin tsige Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar.
Babban-Daraktan MURIC, Farfesa Isiaq Akintola, ya bayyana takaici bisa abin da ya kira shirin gwamnan na fakewa da dalilinsa na tsige wasu sarakunan gargajiya 15 a matsayin hujjar tube Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar.
Sarkin Musulmi shi ne Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Musulunci ta Najeriya da kuma Kungiyar Musulmi ta Jama’atu Nasril Islam (JNI).
A watan Afrilu ne gwamnan ya Aliyu ya tube wasu sarakunan gargajiya 15 kan laifukan da suka danganci rashin tsaro da kuma rikicin filaye a jihar.
Ya ci gaba da cewa, “a kowane lokaci gwamnan na iya far wa kujerar Sarkin Musulmi da dalilin da ya bayar na tube wadancan sarakuna 15 a kwanakin baya.”
managarciya