Home Uncategorized  Tinubu Ya Nada Majalisar Gudanarwa Ta Aikin Hajji, Fitaccen Malamin Sakkwato Ya...

 Tinubu Ya Nada Majalisar Gudanarwa Ta Aikin Hajji, Fitaccen Malamin Sakkwato Ya Shiga Ciki

7
0

 

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da nadin sabuwar majalisar gudanarwa ta hukumar jin dadin Alhazai ta kasa (NAHCON).

Majalisar dattawan Najeriya ce za ta tabbatar da sabbin nade-naden. 
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Ajuri Ngelale, kakakin shugaban kasa ya saki a yammacin ranar Laraba, 10 ga watan Janairu. 
Sanarwar ta ce Tinubu ya nada mutanen ne a cikin “kudurinsa na tabbatar da aikin Hajjin 2024 ya tafi daidai ba tare da matsala ba.” Ga jerin mutanen da aka nada a hukumar aikinb hajjin: Jalal Arabi — Shugaba (a ofis)
Prince Anofi Elegushi — Kwamishinan ayyuka
Aliu Abdulrazaq — Kwamishinan manufofi, ma’aikata da kudi
Farfesa Abubakar Abubakar Yagawal — Kwamishinan tsare-tsare da bincike.
Wakilan yankin
Muhammad Umaru Ndagi — Arewa ta tsakiya
Abba Jato Kala — Arewa maso Gabas
Zainab Musa — Kudu maso Kudu
Farfesa Musa Inuwa Fodio — Jama’atul Nasril Islam
Sheikh Muhammad Bin Othman — Arewa maso Yamma
Tajudeen Oladejo Abefe — Kudu maso Yamma
Aishat Obi Ahmed — Kudu maso Gabas
Farfesa Adedimeji Mahfouz Adebola — Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here