Home Uncategorized Tinubu Ya Amince da Yi Wa Ma’aikata Karin Albashi

Tinubu Ya Amince da Yi Wa Ma’aikata Karin Albashi

10
0

 

Gwamnatin Tarayya ta sanar da yin ƙarin albashi ga ma’aikatanta da kaso 25% zuwa kaso 35%. Ma’aikatan da gwamnatin tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu ta yi wa ƙarin albashi sun haɗa da masu karɓar albashi na bai-ɗaya na CONPSS, CONRAISS, CONPOSS, CONPASS, CONICCS da CONAFSS.

Jaridar NTA ta ce hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na hukumar kula da albashi ta ƙasa, Emmanuel Njoku, ya fitar a ranar Talata, 30 ga watan Janairun 2024. 
Hakazalika gwamnatin tarayya ta yi ƙarin albashi ga ƴan fansho da kaso 20% zuwa kaso 28% a kan albashinsu na yanzu.
 Emmanuel Njoku ya bayyana cewa ƙarin albashin zai fara aiki ne daga ranar, 1 ga watan Janairun 2024. A kwanakin baya ne dai gwamnatin tarayya ta yi ƙarin albashi ga ma’aikatan makarantun gaba da sakandare da ɓangaren lafiya. 
Wannan ƙarin albashin dai na zuwa ne ana a yayin da ake shirin bikin ranar ma’aikata ta duniya a ranar Laraba, 1 ga watan Mayun 2024.
Gwamnatin tarayya ta sha samun kiraye-kiraye daga ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa (NLC) a kan ta yi wa ma’aikata ƙarin albashi saboda tsadar rayuwar da ake fama da ita, sakamakon cire tallafin man fetur. 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here