Tambuwal Ya Sassauta Dokar Hana Fita a jihar Sakkwato

Tambuwal Ya Sassauta Dokar Hana Fita a jihar Sakkwato

 

Gwamnan jihar Sakkwato Aminu Waziri Tambuwal, biyo bayan bayanin da jami'an tsaro  suka yi masa ya bayar da umurnin a sassauta dokar hana fita da aka sanya a birnin Sakkwato.

 Bisa ga wannan umurnin, yanzu an hana fitar ne daga faɗuwar rana zuwa wayewar gari a birnin Sakkwato da kewaye. 
Kuma an yi hakan ne domin a baiwa mutane dama su fita neman abinci da sauran sana’o’in su. 

A sanarwar da Kwamishinan Yada labarai Isah Bajini Galadanchi ya fitar a ranar litinin  ya ce saboda haka gwamnati na bada shawara a gare mu da mu tabbatar da zaman lumana a tsakanin mu, domin ba za a lamunce ma duk wani nau'in taka doka da oda ba a wannan jaha.