Tambuwal Ya Nemi Buhari Ya Aiyana Dokar Tabaci Kan 'Yan Ta'adda

Tambuwal Ya Nemi Buhari Ya Aiyana Dokar Tabaci Kan 'Yan Ta'adda
Buhari da Tambuwal

Gwamnan jihar Sakkwato Aminu Waziri Tambywal ya bukaci shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aiyana dokar tabaci a dukkan yankunan da 'yan ta'adda suka mamaye.
A cewar Tambuwal ya gana da shugaban kasa Buhari a fadar gwamnatin Nijeriya da marecen Litinin kusan minti 30  ya ce aiyanawar za ta karawa sojojin Nijeriya kaimi a hare-hare da suke kaiwa.

Kaddamar da hare-haren zai taimaka kwaran gaske a jihohin da batagarin suka addaba kamar Sakkwato da Zamfara da Katsina da Kaduna da Neja da Kebbi. 
Tambuwal ya roki shugaba Buhari a samar da karin kayan aiki ga jami'an tsaro a dauki karin sojoji don ana da bukatarsu sosai.