Tambuwal Ya Baiwa Mutum 64 Mukami Domin Su Taimakwa Aikinsa Na Sanata

Tambuwal Ya Baiwa Mutum 64 Mukami Domin Su Taimakwa Aikinsa Na Sanata

 

Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya baiwa mutum 64 mukaman mataimaka na musamman da masu ba da shawara a bangarori daban daban na aikin majalisa dattijai da yake yi.

Sanata Tambuwal ya ba da mukaman ne ga 'yan asalin kananan hukumomi bakwai  da yake wakilta a majalisar Dattijai. 

Wannan yana cikin kudirinsa na samar da aiki ga mutanen yankinsa kamar yadda yake cewa.

Sanata Tambuwal ya nada masu bashi shawara 15, mataimaka na musamman a fannoni daban-daban guda 49 da suka fito a karamar hukumar Bodinga, Tureta, Dange Shuni, Tambuwal, Kebbe, Shagari da Yabo.

Tambuwal a takardar da ofishin yada labaransa suka fitar ya yi kira ga wadan da ya  baiwa mukaman da su yi kokarin saukar da nauyin da aka daura musu.