Home Uncategorized Sokoto: Hari Marar Dadi ‘Yan Bindiga Sun Kona Mace Da Surukarta Da...

Sokoto: Hari Marar Dadi ‘Yan Bindiga Sun Kona Mace Da Surukarta Da ‘Ya’yanta Biyu

8
0

 

Wasu miyagu da ake kyautata zaton ƴan bindiga ne sun ƙona wata mata da surukarta da kuma ƴaƴanta biyu da ransu a wani harin da suka kai a jihar Sokoto. 

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ƴan bindigan sun kai harin ne a ƙauyen Kurya da ke ƙaramar hukumar Rabah a jihar Sokoto da misalin ƙarfe 8:30 na daren ranar Lahadi. 
Rahotanni sun ce ƴan bindigan sun kashe mutanen ƙauyen 12 tare da sace mata uku a yayin harin. 
Wani mazaunin yankin, Yusuf Garba ya ce ɗaya daga cikin wadanda aka sace ta rasa mijinta a harin, rahoton Trust Radio ya tabbatar. 
“Daga cikin wadanda aka kashe akwai wata mace ɗaya da aka ƙona ta mutu tare da surukarta da ƴaƴanta biyu a cikin ɗakinsu.” A cewarsa. 
A cewarsa, daga baya maharan sun yi wani ƙazamin faɗa da sojoji. “Muna zargin su ma sun yi asara mai yawa saboda mun ga tabon jini a inda suka ajiye babura. Amma ka san ba sa barin gawarwakinsu a baya.” A cewarsa. 
Sai dai rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar da mutuwar mutum bakwai ne a yayin harin. 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here