Sojoji Sun Kama Manyan Masu Garkuwa Da Mutane Biyu
Dakarun Operation Safe Haven sun kashe wasu kasurguman masu garkuwa da mutane biyu sannan sun kama masu fashi da makami biyu tare da ceto matafiya tara a yankin arewacin kasar.
Daraktan labarai na ayyukan tsaro, Manjo Janar Benard Onyeuko, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya saki a ranar Talata, 12 ga watan Yuli, Channels TV ta rahoto.
Ya yi bayanin cewa sun samu nasara a ayyukan da suka gudanar tare da jami’an yan sanda a tsakanin Alhamis da Asabar na makon da ya gabata a kokarinsu na ganin an yi bikin sallah cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali.
A cewar kakakin rundunar sojin, wadanda ake zargin sun kuma bayyana wani Mallam Buhari Umar a matsayin shugaban kungiyarsu.
Yan bindigar sun farmaki gidan Reverend Daniel Umaru na cocin EYN a Njairi da ke karamar hukumar Mubi inda suka harbe shi sannan suka kashe yaransa biyu da kuma sace diyarsa mai shekaru 13.
managarciya