Shugaba Buhari zai tafi ƙasar Habasha a ranar Litinin

Shugaba Muhammadu Buhari zai tafi kasar Habasha waton Ethopia  domin halartar taron rantsar da Firai Ministan kasar Abiy Ahmed a wa'adinsa na biyu da za a yi a yi a ranar Litinin a birnin Addis Ababa.

Shugaba Buhari zai tafi ƙasar Habasha a ranar Litinin
'Yan Bindiga Suna Karɓar Shinkafa da taliya matsayin Kudin Fansa domin yunwa ta kama su a daji

Shugaba Buhari zai tafi ƙasar Habasha a ranar Lahadi

Daga : Janaidu Amadu Doro.

Shugaba Muhammadu Buhari zai tafi kasar Habasha waton Ethopia  domin halartar taron rantsar da Firai Ministan kasar Abiy Ahmed a wa'adinsa na biyu da za a yi a yi a ranar Litinin a birnin Addis Ababa.

Shugaba Buhari dai zai bar birnin Abuja a gobe Lahadi zuwa babban birnin Habasha kuma zai gabatar da jawabin fatan alheri a taron rantsuwar.

Ana sa ran kuma daga nan zai halarci liyafar cin abinci tare da sauran shuwagabannin ƙasashe.

Daga cikin wadanda za su mara wa Shugaban kasar baya a tafiyar akwai : ministan harkokin ƙasashen waje Geoffery Onyeama da Shugaban Hukumar Leƙen Asiri ta NIA Ambasada Ahmed Rufai Abubakar da sauransu.

Bayan kammala bukukuwan rantsuwar shugaban zai dawo gida Najeriya a ranar Talata mai zuwa.

Allah ya sa a je lafiya Kuma a dawo lafiya.