Sarkin Kano ya halarci bikin cikar Gambia shekaru 60 da samun ƴancin kai

Sarkin Kano ya halarci bikin cikar Gambia shekaru 60 da samun ƴancin kai

A jiya Litinin ne mai martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II, ya isa birnin Banjul, babban birnin kasar Gambia, a wata ziyarar aiki ta kwanaki biyu.

A wata sanarwa da ta fito daga masarautar Kano, ta ce ziyarar ta biyo bayan gayyatar shugaban kasar Gambia, Adama Barrow.

Sanarwar ta ce, an gayyaci Sanusi ne a matsayin babban bako na musamman a wajen bikin cika shekaru 60 da samun ‘yancin kai na jamhuriyar Gambia.

Ministoci da wasu jiga-jigan gwamnati da suka karbi bakuncinsa sun tarbe shi a lokacin da ya isa filin jirgin sama na birnin Banjul. 

Daga bisani kuma da yammacin ranar, Sarkin ya bi sahun shugaba Barrow da uwargidan sa, Fatumatou Bah Barrow a wata liyafa da aka gudanar a wani bangare na bikin cika shekaru 60 na Gambiya. 

Babban bikin ya  ci gaba da gudana a yau Talata tare da fareti na musamman da sojojin kasar Gambia su ka yi a dandalin Banjul Grande. 

Sanarwar ta kara da cewa ana sa ran Sarki Sanusi zai dawo gida a yau.